15 Yuni 2025 - 23:25
Source: ABNA24
IRGC: Cibiyoyin Leken Asirin Isra’ila Su Ne Hadafi A Kashi Na Uku Na Harin Tabbataccen Alkawari 3

Magoya bayan wannan gwamnatin ta muggan laifuka ya kamata su sani cewa za a ci gaba da gudanar da ayyuka masu inganci da niyya a kan muhimman wuraren wannan gwamnatin karyar har sai an ruguza ta.

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun yi bayani cewa: Muna sanar da al'ummar Iran ma'abota girma da daukaka cewa, sojojin gwamnatin sahyoniyawan azzalumai masu zubar da jini da ke cikin rudu sun ci gaba da kai hare-hare da munanan ayyukan da suke yi a kan Iran din Musulunci. Haka nan kuma ta sake bayyanar da mugunyar ta ta'addanci ta hanyar kai hare-hare ga masoya a wuraren zama tare da kashe wasu sojojin Gum Nam na Imamin Zamani (As) da kwamandojin mujahidan leken asiri, shahidai Mohammad Kazemi, Hassan Mohaqiq da Mohsen Bagheri.

Mayakan IRGC Aerospace Force, suna ci gaba da yin martaninsu mai murkushewa, musamman na daukar fansa kan laifuffukan da gwamnatin 'yan ta'adda suka aikata a yau, sun kai wani sabon hari na makamai masu linzami, inda suka kai hari kan cibiyoyin leken asiri na gwamnatin 'yan mamaya a matsayin kashi na uku na aikin Alkawarin Gaskiya 3.

Magoya bayan wannan gwamnatin ta muggan laifuka ya kamata su sani cewa za a ci gaba da gudanar da ayyuka masu inganci da niyya a kan muhimman wuraren wannan gwamnatin karyar har sai an ruguza ta.

Your Comment

You are replying to: .
captcha